Mahaukaci ya hallaka mutum 8 a Adamawa

Wani mai tabin hankali ya kai farmaki inda ya kashe mutane takwas tare da raunata wasu da dama a unguwar Kate-Gamji da ke unguwar Libbo a karamar hukumar Shelleng a jihar Adamawa.

An bayyana cewa mutumin mai suna Ali Denham, ya yi amfani da wuka ne wajen far wa wasu mazauna garin a daren ranar Laraba, inda ya kashe mutane takwas tare da raunata wasu uku kafin daga bisani wasu su kashe shi.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin a ranar Asabar, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa, Sulaiman Nguroje, ya gargadi iyalai kan ajiye mahaukata a gida lokacin da ya kamata a kwantar da su a asibitocin masu tabin hankali.

Ya ce ‘yan sanda sun fara bincike kan lamarin. A halin da ake ciki, shugaban karamar hukumar Shelleng, Abubakar Musa Abba, ya kai ziyarar jaje ga iyalan wadanda suka rasu, inda ya bukace su da su dauki asarar da suka yi a matsayin daga Allah.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...