Likitoci sun janye yajin aiki da su ke a fadin Najeriya

Mambobin kungiyar NARD ta  likitoci masu neman kwarewa sun janye yajin aikin sai baba ta gani da su ke yi bayan da suka cimma yarjejeniya da gwamnatin tarayya.

A ranar 1 ga watan Nuwamba ne, Muhammad Sulaiman shugaban kungiyar ya sanar da cewa kungiyar ta tsunduma yajin aikin sai baba ta gani.

Likitocin sun bukaci a rika biyansu albashi mai kyau, biyan bashin karin albashin da suke bin gwamnati, inganta yanayin aikinsu, samar da karin ma’aikata da kuma samar da kayayyakin da suka zama wajibi wajen kula da lafiya.

Har ila yau damuwar likitocin ta haÉ—a da yadda aiki ya yi musu yawa inda suka ce hakan na shafar ingancin kula da lafiyar al’umma a Najeriya.

A wani sako da ya wallafa a ranar Asabar,a shafinsa na X da aka fi sani da Twitter a baya Sulaiman ya tabbatar da dakatar da yajin aikin.

Ya ce an dauki matakin janye yajin aikin ne biyo bayan wasu jerin tarukan sulhu da akayi da shugabannin kungiyar da wakilan gwamnatin tarayya inda aka rattaba hannu kan wata yarjejeniyar fahimtar juna.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) Æ™arÆ™ashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da Æ™arar da É—an majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]