Lakurawa sun kashe mutane 33 a jihar Kebbi

Yan ta’addan Lakurawa sun kashe akalla mutane 33 a yayin da su ka kai wasu jerin hare-hare kan al’ummomi da dama dake ƙaramar hukumar Arewa ta jihar Kebbi.

Ƴan ta’addar sun ƙaddamar da kai hare-haren ne a ranar Laraba.

A wata sanarwa da aka fitar ranar Alhamis, Bashir Usman mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Kebbi ya ce yan ta’addan sun farma garuruwan ne domin satar shanu amma sai su ka fuskanci turjiya daga mutanen.

Ya kara da cewa yan ta’addar sun shigo garuruwan ne daga karamar hukumar Gudu ta jihar Sokoto.

A cewar sanarwar rundunar ta yi matukar rashin jin daɗin mutane da su ka mutu ba su ba su gani ba kana ta miƙa saƙon taaziya ga bakin dayan mutanen dake karamar hukumar Arewa.

“Binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa mayakan Lakurawa ne suka ka shiga yankin domin satar shanu. An yi ittifaƙin cewa sun fito ne daga karamar hukumar Gudu ta jihar Sokoto” a cewar sanarwar.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]