Lagos Ce Birnin Mafi Hatsari A Duniya |VOA

Gwamnatin jihar Legas ta yi watsi da wani rahoto da wani sashen bincike da bin diddigi na mujallar tattalin arziki ta Landon, mai suna Economist Intelligence ta fitar, dake aiyana birnin a matsayin wanda yafi kowane birni rashin tsaro, da hatsari a duniya, daga cikin birane 60 da ta yi nazari akan su.

A wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar Gbenga Omotosho ya
fitar, ya baiyana rahoton a matsayin soki burutsu, kuma mara tushe balle
madafa.

To ko yaya al’ummar jihar ta Legas suka ji da wannan rahoto? A bayanin da suka yiwa wakilin Muryar Amurka, wasun su kamar wani malami, ya ce kokadan bai yarda da wannan rahoto ba, da a kace wai Legas ita ce mafi karancin tsaro a duniya, bayan akwai wasu jihohi da suka fi wannan jiha rashin tsaro.

A can baya ma dai an sha fitar da rahotanni makamantan wannan wanda gwamnati da al’ummar kasa ke baiyana su a matsyain na son kai.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]