Ku San Malamanku Tare da Sheikh Farfesa Mansur Sokoto | BBC Hausa

Bayanan bidiyo,
Ku San Malamanku tare da Farfesa Mansur Sokoto

Fitaccen malamin addinin nan a jihar Sokoton Najeriya Sheikh Farfesa Mansur Sokoto ya ce duk da cewa wasanni na daga cikin abin da ya fi so, to ba ya iya yin su a yanzu saboda a Najeriya akwai abubuwa da yawa da ko yana so to ba zai iya yin su ba.

Malamin ya faÉ—i hakan ne a wata hira ta musamman a shirin Ku San Malamanku na BBC Hausa, inda ya ce a lokacin da yake Sudan da Madina ya yi wasanni da suka haÉ—a da Takwendo da Kung Fu da Iyo wato Swimming.

Sai dai malam ya ce a yanzu ya kan yi wasu wasannin motsa jiki da suka sauwaƙa a gida.

Wane ne Sheikh Muhammad Mansur Ibrahim Sokoto?

An haifi shehin malamin a birnin Sokoto ranar Litinin 13 ga watan Zulqidah shekara ta 1388 bayan Hijira, daidai da 2 ga Maris din 1969.

Ya yi karatun Ƙur’ani a gidansu a wajen mahaifiyarsa Modibbo Hafsatu, wacce ke da makarantar koyar da yara da matan aure.

Ya sauke Ƙur’ani yana da shekara takwas a lokacin yana aji uku na firamare.

Bayan sauke Ƙur’ani sai Ya fara karatun saniN FiÆ™ihu a wajenta inda ya karanta littattafai irin su Usul-din da Ishmawi da Ahlari.

Daga nan sai ya koma wajen mahaifinsa ya ci gaba da karatun Babus Sahwi ya kuma karatun Iziyya.

Bayan anaɗa mahaifinsa limancin ƙauyensu sai ya kasance ba ya samu lokacinsa, sai ya koma makarantar Malam Abbakar Makera Bakane.ya ci gaba da karatun Iziyya.

Daga bisani ya koma wajen Malam Aliyu Muhammad Gidan Kanawa ya karanci littattafai irin su Riyadus Salihin da na Fiqihu kamar Risala, sannan ya kammala da Askari.

Ya kuma yi karatu a makaratantar Malam Muhammad Isa Talata Mafara ya karanta littattafai irin su Ihyaus Sunna da wasu littattafan Sheikh Dan Fodio da kuma wasu kamar Alburda da sauransu.

Malam ya yi karatu a wajen wasu malaman da dama.

Bayanan hoto,
Malam ya yi digiri na biyu da digirin digirgir a fannin Hadisi duk a Danfodio. Yanzu haka ya zama farfesa a ilimin Hadisi a watan Janairun 2019

A ɓangaren boko ya yi firamare a makarantar Magajin Gari One, inda ya kammala a shekarar 1980, sai ya shiga makarantar sakandare ta Technical da ke Rinjin Sambo ya koyi fasaha da ƙere-ƙere.

“Ina iya cewa sau uku na yi sakandire saboda yanayin sauyin karatu,” in ji malam.

“Bayan kammala karatu na je na samu horo a wani kamfanin motoci inda na fara aikin kanikanci har aka dauke ni aiki a UTC Kaduna 1985.

“Daga nan ne na samu gurbin karatu a Jami’ar Fasaha ta Minna don karantar ilimin kimiyyar komfuta da kuma wani gurbin a Kaduna Polytechnic, a cewar malam.

Sai dai sha’warsa ta koma wa karatun addinin Musulunci ta sa ya bar guraben inda ya ya koma makarantar marigayi Malam Bashir Yusuf a Talata Mafara.

Yana can ne sai ya samu gurbin karatu a Islamic African Center Khartoum da ke Sudan kan shari’a.

“Sai na ce ni makarantar sakandare nake son komawa, abin har ya zo ya zama rigima, da Æ™yar aka amince. Wannan ya sa sau uku kenan ina yin sakandare daga SS1 zuwa SS3.”

A shekarar 1990 sai ya samu gurbin karatu a Jami’ar Islamiyya Madina inda ya yi Kwalejin Hadisi daga shekarar 1990 zuwa 1994.

Daga nan ya komwa gida Najeriya ya fara aiki da KwalejinKimiyya ta jihar Sokoto a lokacin, State Poly kenan a yanzu, ya yi shekara biyu har da hidimar Æ™asa, daga nan ya koma Jami’ar Usman Danfodi a 1996.

Malam ya yi digiri na biyu da digirin digirgir a fannin Hadisi duk a Danfodio. Yanzu haka ya zama farfesa a ilimin Hadisi a watan Janairun 2019.

Tambaya mafi sarƙaƙiya

Kamar yadda aka sani malamai kan Sha fama da amsa tambayoyi, to shi ma Farfesa Mansur haka abin yake gare shi.

“Ana samun tambayoyi masu sarÆ™aÆ™iya sosai. Sai dai ni ina da samun shakkar fatwa, idan har ina da shakku sai na ce a ban lokaci na yi bicike ko na tura wajen wani malamin.

“Akwai wata tambaya da aka min tun a shekarun 1990. Wasu matan aure su biyu mijinsu na zuwa ci rani Lagos. Gudar na da ilimi dayar kuma ba ta da shi.

“To lokacin babu waya mijin kan aiko da saÆ™o ne ta hanyar wasiÆ™a. Ita uwargida ita ce ta iya karatu ita ke karantawa idan an aiko saÆ™o.

“Rannan sai ya aiko da wasika uwargida na karantawa sai ta dubi amarya ta ce “me ki kai wa maigida ne?” Me ya faru ya sake ki saki uku?”

“Suka sha koke-kokensu amarya ta tafi gidansu ba wanda ya nemi ganin takarda. Ta yi zaman idda har ta yi aure.

“Mijin nan bai tashi zuwa Sokoto ba har sai da ta haifi yara biyu. Da ya dawo sai ya tarar amarya ba ta nan, ya gane abin da ya faru.

“To a gaskiyar magana da aka kawo batun wajena sai da na tura su kotu aka warware a can, don abin na da sarÆ™aÆ™iya da yawa,” malam ya ce.

Yaushe ya fara da’awa?

Farfesa ya ce ya tashi tare da ‘yan da’awa. Yana hulda da su Adamu Badullahi da Malam Bello Dan Malam. Tun yana Æ™aramar sakandare a shekara 13.

Ya buÉ—e makarantarsa ta farko a 1983, cikin É—alibansa har da fitattun Æ´an siyasa da manyan Æ´an kasuwa.

Amma fara da’awa haÆ™iÆ™a sai bayan da ya kammala digiri a Jami’ar Madina bayan da ya buÉ—e makarantar Hadisi a gidansu. Makarantar na ci gaba har yanzu.

Ya ce “Na fara tafsirin Ƙur’ani a shiyyar Tsamiyar Dila.”

Littattafai

Malam ya rubuta littattafai da dama tun yana É—alibi a Madina. Sannan ya rubuta cikin harshen Hausa da Larabci.

Wasu daga cikin na Hausan sun haÉ—a da:

  • Alkaki da Ruwan Zuma na tarihin Manzon Allah SAW
  • Ƙaddara ta Riga Fata
  • Abin da ya faru a Ƙarbala
  • AÆ™idun Shi’a a Ma’aunin Shari’a
  • Su waye masoyan Ahlul Baiti?
  • Duniya Makaranta
  • Abokin hira

Malam ya fi son abincin gargajiya musamman tuwon shinkafa da miyar kuka da kuma kwaɗon ƙanzo.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...