Kotun Ta Yanke wa Mutum 3 Hukunci Kan Yin Luwadi

Arewacin Najeriya galibi musulmi ne kuma jihohin da ke yankin na amfani da kotunan shari’a wajen hukunta mutanen da suka aikata laifukan da suka hada da zina da wani sabo.

Adam Dan Kafi, shugaban Hisbah na karamar hukumar Ningi da ke Bauchi ya ce an kama mutanen uku ne a ranar 14 ga watan Yuni, kuma aka gurfanar da su a gaban kotun shari’a.

Mutanen da suka hada da wani tsoho mai shekaru 70, duk sun amsa laifinsu duk da cewa ba lauyoyi ne suka tsaya musu ba, in ji Kafi.

Ya ce mai shari’a Munka’ilu Sabo ya yanke musu hukuncin kisa ne a ranar Alhamis, amma za su iya daukaka kara kan hukuncin nan da kwanaki 30.

Duk wani hukuncin kisa da kotunan shari’ar Musulunci za ta zartar a Najeriya na bukatar amincewar gwamnan jihar.

A Najeriya, kamar yawancin sassan Afirka, ana kallon luwadi a matsayin abin da ba za a amince da shi ba.

Najeriya wadda ita ce kasa mafi yawan al’umma a nahiyar Afirka, tana da wata doka da ta ba da damar dauri a gidan yari ga wadanda aka samu da laifin nuna jinsi daya a bainar jama’a da kuma masu auren jinsi daya.

Hukuncin da aka yanke a Bauchi zai kuma iya haskawa a kan matsayin shari’ar Musulunci a kasar da tsarin mulkinta ya yi watsi da addini.

A watan da ya gabata ne wani mawakin Najeriya ya bukaci kotun daukaka kara da ta bayyana hukuncin shari’a a wata jihar da ta sabawa kundin tsarin mulkin kasar. Ana sa ran yanke hukunci kafin Oktoba.

More News

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Wani mutumi ya kashe mahaifiyarsa a kan kudi

Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Osun sun kama wani mazaunin kauyen Kajola da ke kusa da Apomu a jihar mai suna Lukman Adejoju bisa...

Mayaƙan Boko Haram Biyu Sun Miƙa Kansu Ga Sojoji

Rundunar dakarun soja ta ƙasa da ƙasa wato Multi National Task Force(MNJTF) a turance shiya ta 3 dake Monguno a Najeriya ta bayar da...

Sojoji a birnin Ibadan  sun kama Æ´an fafutukar kafa Æ™asar Oduduwa

Dakarun rundunar sojan Najeriya  sun samu nasarar kama wasu mutane masu fafutukar kafa ƙasar Oduduwa a birnin Ibadan na jihar Oyo. Masu fafutukar sanye da...