Kotun daukaka kara ta kori Sanata Tambuwal – AREWA News

Kotun daukaka kara dake Sokoto ta soke zaben sanata, Abubakar Tambuwal mai wakiltar mazabar kudancin Sokoto da kuma na, Aliyu Shehu wakili a majalisar wakilai ta tarayya mai wakilatar kananan hukumomin, Bodinga/Dange Shuni/ Tureta dukkansu yayan jam’iyar APC.

Kotun ta bayar da umarnin bada shedar cin zabe ga Ibrahim Danbaba a matsayin sanata da kuma Balarabe Kakale a matsayin dan majalisar wakilai ta tarayya.

Yan takarar na jam’iyar PDP sun daukaka kara kan hukuncin da kotun sauraren kararrakin zabe tayi da ya tabbatar da zaben sanata Tambuwal da kuma dan majalisa Aliyu Shehu.

Da yake gabatar da hukuncin ranar Laraba, alkalin kotun Federich Oho ya ce daukaka karar Danbaba da Kakale ta yi nasara.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...