Gwamnan Filato Mutfwang ya nufi kotun ƙoli

Gwamnan Jihar Filato Caleb Mutfwang ya nufi kotun koli domin neman hakkinsa bayan kotun daukaka kara ta ƙwace kujerar gwamna daga hannunsa.

Idan ba a manta ba kotun daukaka kara da ke Abuja a ranar Lahadi ne ta kori gwamnan jihar Filato, Mutfwang Manasseh na jam’iyyar PDP.

Ta kuma umarci Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC, da ta amince da Nentawe Goshwe na jam’iyyar All Progressives Congress, APC, a matsayin zababben gwamna a zaben gwamnan da aka yi ranar 18 ga watan Maris.

Mai shari’a Elfrieda Williams-Dawodu, wadda ya jagoranci kwamitin mutum uku a lokacin da take yanke hukunci, ya buga misali da sashe na 177 na kundin tsarin mulkin kasar, inda ya ce Manasseh ba dan takara ne da PDP ta dauki nauyinsa ba a lokacin zaben.

More News

Kotu ta sauke kakakin majalisar Nasarawa

Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke zamanta a Abuja ta kori kakakin majalisar dokokin jihar Nasarawa, Rt. Hon. Ibrahim Balarabe Abdullahi dan jam’iyyar...

Masu cin gajiyar shirin Npower na kokawa game da rashin biyansu

Wasu masu cin gajiyar shirin gwamnatin tarayya na N-Power a ranar Litinin sun koka kan yadda ake ci gaba da biyan su alawus-alawus din...

Tinubu ya sake naɗa Mele Kyari a matsayin shugaban NNPCL

Shugaba Bola Tinubu ya sake nada Malam Mele Kyari a matsayin babban jami’in gudanarwa na kamfanin man fetur na kasa (NNPCL). An bayyana hakan ne...

Ba baƙon abu ba ne don an haifi yaro da haƙori a bakinsa—in ji masana lafiyar yara

Likitocin kula da lafiyar yara sun ce jariran da ke da hakora daya ko biyu a lokacin haihuwa hakan ba baƙon al'amari ba ne. Wannan...