Kotu ta jingine dakatarwar da aka yiwa Kwankwaso daga jam’iyar NNPP

Wata babbar kotu dake Kano ta jingine dakatarwar da aka yiwa, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso daga jam’iyar NNPP.

Da yake yanke hukuncin a ranar Talata alkalin kotun mai shari’a, Usman Naabba ya kuma hana mambobin jam’iyar tsagin da suka dakatar da Kwankwaso ayyana kansu a matsayin shugabannin jam’iyar NNPP.

A makon da yawuce ne kwamitin amitattun jam’iyar ta NNPP ya ayyana dakatar da Kwankwaso daga jam’iyar kan zargin cin amanar jam’iyar.

Amma kuma wani tsagin jam’iyar dake biyayya ga tsohon gwamnan ya janye dakatarwar da aka yi masa.

Har ila yau kotun ta umarci hukumar zabe ta INEC da kada ta yi aiki da dakatarwar har sai an gama sauraren shari’ar.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) Æ™arÆ™ashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da Æ™arar da É—an majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]