Babachir Lawal: Obi Da Kwankwaso Na Da Kashi 70 Cikin 100 Na Lashe Zaɓen 2027



Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Babachir Lawal, ya yi hasashen cewa ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, zai sha kaye a zaɓen 2027.

A wata hira da ya yi da Symfoni TV, Lawal ya ce tikitin Peter Obi da Rabi’u Musa Kwankwaso na jam’iyyar NDC yana da damar kashi 70 cikin 100 na samun nasara, yayin da ya bai wa Shugaba Bola Tinubu damar kashi 50 cikin 100.

Babachir ya ce yana fatan Atiku ya faɗi zaɓen, yana mai zargin cewa zaɓen fidda gwani na ADC da ya ba Atiku tikitin takara ya cika da maguɗi. An dai san cewa Babachir ya fice daga ADC bayan saɓanin da ya yi da Atiku kan batun zaɓen fidda gwanin.

More from this stream

Recomended