
Jam’iyar National Democratic Congress wato NDC ta tabbatar da Peter Obi a matsayin wanda zai yiwa jam’iyar takarar zaben shugaban ƙasa a zaɓukan shekarar 2027.
Jam’iyar ta dauki wannan matakin ne a wurin taronta da aka gudanar a birnin tarayya Abuja a ranar Asabar.
A wurin taron, Victor Umeh sanata dake wakiltar mazaɓar Anambra ta tsakiya shi ne ya gabatar da kudirin da ya nemi a tabbatar da Obi a matsayin wanda zai yiwa jam’iyyar takara inda, Sanata Ovie Omo-Agege tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawa ya goyi bayan kudirin inda nan take wurin ya kaure da ihu da shewa na murna.
A ranar 17 ga watan Mayu ne Obi ya karɓi fom na tsayawa takarar shugaban ƙasa a jam’iyar. Bayan kwanaki uku ne kuma aka tantance shi a matsayin ɗantakara ɗaya tilo wanda zai yi takarar kujerar shugaban ƙasa a jam’iyar.
Da yake magana a wurin karɓar tikitin takarar, Obi ya ce gwamnatinsa za ta magance matsalar rashin tsaro, ilimi da kuma ta tattalin arziki da ake fama da su

