Gwamnan jihar Anambra,Willie Obiano ya tabbatar da cewa mutane 12 ne suka mutu a jihar sanadiyyar cutar Korona.
Gwamnan ya bayyana haka ne cikin wani jawabi na musamman da ya yi daren ranar Litinin domin yi wa mutane karin haske kan yaki da cutar Korona a jihar.
Ya kuma ce ya zuwa yanzu an tabbatar da mutane 101 ne suka kamu da cutar a jihar cikin gwaji 618 da aka yi.
Ya kara da cewa mutane 77 ne suka warke daga cutar a jihar.