Hukumar kula da jin daɗin alhazai ta jihar Kano ta ayyana ranar 14 ga watan Mayun 2026 a matsayin ranar fara jigilar maniyyata daga jihar zuwa ƙasar Saudiyya domin gudanar da aikin Hajjin bana.
Sanarwar ta fito ne ta bakin kakakin hukumar, Sulaiman A. Dederi, inda ya ce shugaban hukumar, Abubakar Ibrahim Matawalle, ya bayyana hakan ne yayin rufe taron bita kan shirye-shiryen Hajji da aka gudanar a makarantar koyar da Larabci da ke Kano.
Matawalle ya bayyana cewa an ɗauki wannan mataki ne bayan fitar da jadawalin aikin Hajji daga hukumar alhazai ta ƙasa. Ya kuma ƙara da cewa an zaɓi kamfanin jiragen sama na Max Air domin jigilar maniyyatan jihar.
Shugaban ya jaddada cewa hukumarsa ta kammala dukkan shirye-shiryen da suka dace domin tabbatar da cewa an kwashe maniyyata cikin aminci.
Haka kuma, hukumar ta buƙaci maniyyata su ci gaba da nazarin abubuwan da aka koyar da su, domin su gudanar da ibadar Hajji yadda ya kamata. An kuma shawarce su da su bi dokokin da hukumomin Saudiyya da Najeriya suka gindaya.
A wani ɓangare, an riga an fara jigilar maniyyata a ƙasar, inda a ranar Lahadi aka fara da maniyyata 474 daga jihar Kogi, waɗanda suka tashi daga filin jirgin saman Abuja.
Kano Ta Sanya Ranar Fara Jigilar Maniyyata Zuwa Hajjin 2026

