Iran Ta Kai Hari Kan Sansanin Sojin Amurka A Qatar

Ma’aikatar tsaron ƙasar Qatar ta bayyana cewa Iran ta kai hari da makamai masu linzami kan sansanin sojin Amurka da ke ƙasar.

A cikin sanarwar da ta fitar, ma’aikatar ta ce Qatar ta samu nasarar kaɓo ɗaya daga cikin makaman masu linzamin da aka harba. Sai dai ɗaya daga cikin makaman ya faɗa cikin sansanin sojin Amurka da ke Al Udeid, wanda ake bayyana a matsayin mafi girman sansanin Amurka a yankin Gabas ta Tsakiya.

Hukumomin Qatar sun tabbatar da cewa ba a samu asarar rayuka ba, kuma babu wanda ya jikkata sakamakon harin.

Har yanzu dai ba a bayyana ƙarin bayani kan dalilin harin ko matakan da za a ɗauka ba.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]