Iran Ta Kai Hari Kan Sansanin Sojin Amurka A Qatar

Ma’aikatar tsaron ƙasar Qatar ta bayyana cewa Iran ta kai hari da makamai masu linzami kan sansanin sojin Amurka da ke ƙasar.

A cikin sanarwar da ta fitar, ma’aikatar ta ce Qatar ta samu nasarar kaɓo ɗaya daga cikin makaman masu linzamin da aka harba. Sai dai ɗaya daga cikin makaman ya faɗa cikin sansanin sojin Amurka da ke Al Udeid, wanda ake bayyana a matsayin mafi girman sansanin Amurka a yankin Gabas ta Tsakiya.

Hukumomin Qatar sun tabbatar da cewa ba a samu asarar rayuka ba, kuma babu wanda ya jikkata sakamakon harin.

Har yanzu dai ba a bayyana ƙarin bayani kan dalilin harin ko matakan da za a ɗauka ba.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]