INEC za ta gudanar da zaben gwamnonin Kogi da Bayelsa

Farfesa Mahmoud
Image caption

Tun da fari INEC ta sanya watan Nuwamba mai zuwa a matsayin lokacin zaben gwamnonin jihohin Kogi da Bayelsa

A Najeriya hukumar zabe mai zaman kan ta, ta sanya lokacin da za a gudanar da zaben gwamna a jihohin Kogi da Bayelsa.

Wannan na kunshe cikin sanarwar da INEC ta aike wa manema labarai.

A ranar tara ga watan Afirilu da ya wuce ne INEC ta fitar da jadawalin yadda zaben zai kasance a ranar biyu ga watan Nuwamba mai zuwa.

Daga bisani hukumar ta yi ta samun kiraye-kiraye daga gwamnati, da majalisu da shugabannin al’umma har da na addinai daga jihar Bayelsa kan a sauya lokacin saboda ya zo dai-dai da ranar addu’ar shekara-shekara da ake gudanarwa tun daga shekarar 2012.

Bayan nazari da tuntubar juna, hukumar zaben ta sanar da ranar Asabar 16 ga watan nan a matsayin ranar da za a gudanar da zaben gwamna a jihohin Kogi da Bayelsa.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...