Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta bayyana cewa kusan ma’aurata ɗari bakwai da ashirin sun kammala gwaje-gwajen lafiya a shirye-shiryen bikin auren gama-gari da gwamnatin jihar ke shirin gudanarwa.
Mataimakin Babban Kwamandan Hukumar, Mujahideen Aminudddeen, ya ce ana ci gaba da aikin tantancewar a ƙananan hukumomi daban-daban na jihar.
A cewarsa, gwaje-gwajen sun haɗa da na cutar kanjamau (HIV/AIDS), ciwon hanta nau’i na B, daidaituwar jinsin halitta, amfani da miyagun ƙwayoyi da sauran cututtuka masu yaɗuwa ta hanyar saduwa.
An shirya bikin ne domin taimaka wa zawarawa, waɗanda aka sake, marayu da sauran marasa galihu. Gwamnatin Jihar Kano za ta ɗauki nauyin wasu daga cikin kuɗaɗen aure tare da ba da tallafin rayuwa ga ma’auratan.
Hisbah Ta Yi Gwajin Lafiya Ta Mutane Sama Da 700 Gabanin Auren Bai-Ɗaya A Kano

