Gwamnatin tarayya ta hana sayar da iskar gas ƙasashen waje

Gwamnatin tarayya ta sanar da hana sayar man iskar gas na LPG da ake girki da shi ya zuwa ƙasashen waje.

Ekperikpe Ekpo ƙaramin ministan harkokin mai ɓangaren iskar gas shi ne ya sanar da haka ranar Alhamis a lokacin wani taron masu ruwa da tsaki.

Ya ce matakin an ɗauke shi ne da gangan domin tabbatar da wadatuwar iskar a kasuwar cikin gida da kuma sauƙaƙawa mutane saboda yadda gas ɗin yayi tsada.

Ya ƙara da cewa tabbas idan aka samu wadatuwar iskar gas ɗin to kuwa babu makawa farashinsa zai yi ƙasa.

” Ina magana da hukumar NMDPRA dake saka ido muna yin taruka kusan kullum da kuma kamfanonin da suke samar da gas irinsu Shell,Mobil da Cheveron akwai fatan cewa abubuwa za su canza. Bama buÆ™atar muyi ta surutu akan batun.” Ya ce

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...