Gwamnatin Kano za ta dawo da tsarin kai ƴan jihar kasashen waje don karatu

Gwamnatin jihar Kano ta dawo bayar da tallafin karatu na gaba da digiri na biyu ga ‘yan asalin jihar.

An bayyana hakan ne a ranar Juma’a ta wata sanarwa mai dauke da sa hannun sakataren gwamnatin jihar Kano, Dakta Abdullahi Baffa Bichi.

Ana kira ga daliban da suka kammala karatun digiri na farko waɗanda suka fito daga jihar kuma suke da ƙoshin lafiya don tafiya ƙasashen waje.

Ya kuma bayyana cewa karo na karshe da jihar ta bayar da irin wannan tallafin shi ne a shekarar 2025, lokacin gwamnatin Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]