Gwamnatin Kano za ta dawo da tsarin kai ƴan jihar kasashen waje don karatu

Gwamnatin jihar Kano ta dawo bayar da tallafin karatu na gaba da digiri na biyu ga ‘yan asalin jihar.

An bayyana hakan ne a ranar Juma’a ta wata sanarwa mai dauke da sa hannun sakataren gwamnatin jihar Kano, Dakta Abdullahi Baffa Bichi.

Ana kira ga daliban da suka kammala karatun digiri na farko waɗanda suka fito daga jihar kuma suke da ƙoshin lafiya don tafiya ƙasashen waje.

Ya kuma bayyana cewa karo na karshe da jihar ta bayar da irin wannan tallafin shi ne a shekarar 2025, lokacin gwamnatin Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]