Kotun Majistare ta 2 da ke Kano ta fara sauraron shari’ar TikToker Fatima Abdullahi, wadda aka fi sani da Fati Cele, bisa zargin kashe saurayinta Isma’il Sidi, wanda aka fi sani da Isma’il Buzu.
An karanta mata tuhume-tuhumen da ake yi mata, inda ta musanta su. Lauyanta ya nemi a ba ta beli saboda raunukan ƙonewa da ta samu a hannaye, ƙafafu da fuska, amma masu gabatar da ƙara sun ce kotun ba ta da hurumin bayar da beli a irin wannan shari’a.
Kotun ta ɗage ci gaba da sauraron shari’ar zuwa ranar 20 ga Yuli, 2026, tare da umarnin a ci gaba da tsare Fati Cele yayin da ake ba ta kulawar lafiya.
‘Yan sanda sun ce bincikensu ya nuna cewa rikici ya barke tsakanin Fati Cele da marigayin kafin mutuwarsa. Sun kuma yi zargin cewa ta banka wa gidan wuta domin lalata shaidu da kuma kawo cikas ga bincike.
Kotu a Kano Ta Fara Sauraron Shari’ar Ƴar Tiktok Fati Cele Kan Zargin HaIIaka Saurayinta

