Gwamnan Bauchi ya kirkiri sababbin masarautu 13 a jihar

Sulaiman SaadHausa9 months ago

Gwamnan jihar Bauchi,Bala Muhammad ya rattaba hannu kan sabuwar dokar nadi da kuma sauke sarakuna wacce ta bayar da dama ƙirƙirar sababbin masarautu 13 da kuma gundumomi 111 a fadin jihar.

Har ila yau gwamnan ya sanya hannu kan gyaran dokar Masarautar Sayawa inda aka samar da Masarautar Zaar dake da hedkwata a  garin Mhrim Namchi dake karamar hukumar Tafawa Balewa ta jihar.

Masarautun da dokar ta samar sun hada da Masarautar Burra dake da hedkwata  Burra, Masarautar Duguri dake da hedkwata a Yuli, Masarautar Dambam dake da hedkwata a Dambam, Masarautar Bununu dake da hedkwata a Bununu, Masarautar Lere dake da hedkwata a Lere, Masarautar Darazo dake da hedkwata a Darazo, Masarautar Jama’a dake da hedkwata Nabardo.

Sauran sun hada da Masarautar Lame dake da hedkwata a  Gumau, Masarautar Toro dake da  hedkwata a Toro, Masarautar Ari  dake da hedkwata a Gadar Maiwa, Masarautar Warji dake da hedkwata a Katangar Warji, Masarautar Giade dake da hedkwata a Giade da kuma Masarautar Gamawa dake da hedkwata a  Gamawa. Masarautar Sayawa Zaar dake da hedkwata a Mhrim Namchi.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...