Gwamna Yusuf Ya Yi Allah-Wadai Da Halayyar Wasu Matasa A Kano

Gwamnan Jihar Kano, Abba Yusuf, ya yi kakkausar suka kan halayyar wasu matasa da suka aikata abin da ya kira rashin da’a yayin ziyarar uwargidan shugaban kasa, Sanata Oluremi Tinubu.

A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Mustapha Muhammad, ya fitar, gwamnan ya bayyana lamarin a matsayin abin kunya da ba za a amince da shi ba, yana mai cewa bai wakilci al’adu da dabi’un mutanen Kano ba.

Yusuf ya bayyana hakan ne yayin wani taron addu’a na musamman karo na uku da aka gudanar a gidan gwamnati, inda masu karatun Alkur’ani 4,444 suka halarta domin neman zaman lafiya da ci gaba.

Ya ce halayyar matasan ta saba da manufar gwamnatin sa da kuma koyarwar addinin Musulunci da ke karfafa ladabi da girmamawa.

More from this stream

Recomended