EFCC ta kama masu sayen kuri’a a zaben gwamnan Anambra

Sulaiman SaadHausa9 months ago

Hukumar EFCC dake yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta’annati tace jami’anta sun  kama wasu mutane uku da ake zargi da sayen kuri’a a zaben gwamnan jihar Anambra da aka yi a ranar Asabar.

A wata sanarwa da ta watsa ranar Asabar a shafinta na X da aka fi sani da Twitter a baya EFCC  ta ce jami’anta ne dake sanya ido kan yadda zaben yake guda suka kama mutanen a sassan jihar daban-daban.

” Mutanen da aka kama sun hada da Emeka Ilokasia wanda aka kama a mazaba ta 2 a karamar hukumar Njikoka Anambra da Nwachukwu Loretta da aka kama a mazaba ta 2, Awkuzu akwati mai namba OO8 a karamar hukumar Oyo da kuma Emuka Chukwudi da aka kama a kauyen Umunachi karamar hukumar Danukofia,” a cewar sanarwar.

“Dukkanin mutanen an kama su ne a lokacin zaɓen gwamnan jihar Anambra na ranar 08 ga watan Nuwamba na shekarar 2025,”

Hukumar ta kara da cewa za a gurfanar da mutanen a gaban kotu da zarar an kammala bincike.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...