A halin yanzu dai tsohon gwamnan babban bankin Najeriya Godwin Emefiele yana tsare a hannun hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa.
An tabbatar da cewa, Emefiele, wanda a halin yanzu ake yi masa tambayoyi a hedikwatar hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasa, Jabi, Abuja, jami’an hukumar EFCC sun kama shi a daren ranar Alhamis, kasa da sa’a guda bayan ya dawo daga kurkukun ƴan sandan farin kaya
Wata majiya mai tushe ta bayyana hakan a safiyar Juma’a, inda ta bayyana cewa hukumar EFCC na binciken Emefiele kan zarginsa da aikata ba daidai ba a wa’adinsa na shugaban babban bankin Najeriya.
“Eh, a halin yanzu Emefiele yana hannunmu (EFCC); an kama shi ne a daren jiya kasa da sa’a guda bayan hukumar DSS ta sako shi. A halin yanzu ana yi masa tambayoyi a hedikwatarmu, yayin da ake bincikensa kan zargin almubazzaranci da wasu abubuwa lokacin yana gwamnan CBN,” inji majiyar.