Dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party a zaben 2023, Yusuf Datti Baba-Ahmed, ya sake nanata cewa jam’iyyar APC ba ta lashe zaben shugaban kasa na shekarar ba.
Datti ya bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da shi a shirin Politics Today na tashar Channels Television.
Ya amince cewa kotuna sun yanke hukunci kan zaben, amma ya ce hakan bai canja ra’ayinsa ba game da sakamakon.
Datti ya kuma ce har yanzu yana kan bakansa na gargadin da ya yi a baya cewa amincewa da sakamakon zaben na iya shafar dimokuradiyya.
Ya zargi gwamnati da gazawa a fannoni masu muhimmanci kamar tsaro da tattalin arziki, yana mai cewa tana mai da hankali kan raunana jam’iyyun adawa.
Datti Baba-Ahmed Ya Ce APC Ba Ta Ci Zaben 2023 Ba

