Cutar Ebola ta fara bazuwa makwabta

wasu ma'aikatan lafiya a asibitin Ebola

Hakkin mallakar hoto
Reuters

Image caption

Kusan mutane 1,400 cutar Ebola ta kashe kwanan nan a Jamhuriyar Dumokuradiyyar Kongo

Hukumar Lafiya ta Duniya ta tabbatar cewa annobar cutar Ebola wadda ta barke a Jamhuriyar Dumokuradiyyar Kongo, ta bazu zuwa makwabciyar kasar, Uganda.

Ma’aikatar lafiya ta Uganda da Hukumar Lafiya ta Duniya sun ce, a yanzu haka ana yi wa wani yaro dan shekara biyar wanda ya fito daga Kongon ya tsallaka zuwa Uganda wanda kuma yake dauke da cutar, magani.

Yaron ya shiga Uganda ne tare da sauran ‘yan uwansa , ranar 9 ga watan nan na Yuni, kuma a yanzu ana masa magani a wani asibiti da ke bangaren Uganda ta iyakar kasashen biyu.

  • Bincike: Masu cutar Ebola na samin tabin hankali
  • Gwamnati ta tuhumi Sheikh El-Zakzaky da laifin kisan kai

Daman dai wannan bazuwa ta cutar Ebola daga Jamhuriyar Dumokuradiyyar Kongo zuwa wata kasa makwabciya, abu ne da aka dade ana tsammani, musamman ganin yadda aka jima ana ta gargadi da ankarar da jama’a, sai kuwa ga shi kwatsam ta tabbata.

Tuni dai aka tura masu bayar da agajin gaggawa kan cutar, zuwa wannan yanki domin gano ko akwai wani da shi ma ya kamu da ita ko yake cikin hadarin kamuwa da cutar.

Daman tuni hukumomin Ugandar da hadin guiwar kungiyar agaji ta Save the Children sun ce sun riga sun ba wa ma’aikatan lafiya da masu aikin sa-kai hadi da malaman makaranta sama da dubu hudu horo da riga-kafin cutar, da kuma ba su kayayyakin aiki na maganinta ko da ta ka iya kunno kai kasar.

A shekarar da ta wuce ne annobar cutar mai saurin kisa ta barke sosai a Jamhuriyar Dumokuradiyyar Kongo, kuma zuwa yanzu ta hallaka sama da mutane 1400, bayan wasu sama da 2000 da ta kama.

A yau Laraba ne za a yi wani zama na tattaunawa tsakanin jami’an Jamhuriyar Dumokuradiyyar Kongon da Uganda, domin yanke shawarar ko za a kai ‘yan uwan yaron wadanda suke Uganda zuwa wata cibiya ta musamman kan cutar a Kongon domin sanya ido a kansu.

Cutar Ebola dai tana haddasa zubar da jini a cikin mutum da zazzabi mai karfi da kuma amai.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...