An bai wa dan dambe suna Coronavirus | BBC Hausa

An bai wa dan damben gargajiya suna Coronavirus

An bai wa Abdullahi Ali matashin dan wasan damben gargajiya da ke dambatawa a jihar Kano da ke Najeriya suna ”Coronavirus”.

An haifi Abdullahi a Kurna babban layi da ke karamar hukumar Ungoggo, amma yana zaune a Kunya karamar hukumar Minjibir a jihar Kano.

Abdullahi ya fara wakiltar Kudu, a kuma bara ne sunansa ya kara fita a harkar damben gargajiya.

Hakan ya sa ya fara amsa sunan Autan Dan Alin bata isarka, wani shahararren dan damben Kudu wanda ke kan lokaci.

Autan Dan Ali ya nemi amincewar mahaifiya a wannan sana’ar da yake yi ta kuma amince masa tare da yi masa addu’ar samun nasara.

Matashin dan wasan mai shekara 20, ya gagari sa’anninsa a harkar damben gargajiya, suna jin tsoron yin wasa da shi.

Autan Ali yana daga cikin ‘yan damben da ya yi kisa da yawa a filin wasa na Ado Bayero Square a bara.

Bayan Shagon Dan Aliyu da Bahagon Mai Takawasa, sai Autan Dan Ali da ya yi kan-kan-kan da yawan kisa tare da sarkin dambe Garkuwan Cindo.

Kwazon da yake yi ne Sarkin masu shirya wasan damben gargajiya na Najeriya, Mamman Bashar Danliti ya saka masa suna coronavirus.

Danliti shugaban kungiyar damben jihar Kano ya ce dan wasan jarimi ne zai kuma yi fice da suna a damben gargajiya.

Ya kara da cewar Abdullahi na zuwa makaranta da safe, sannan ya je filin dambe da yammaci, sannan ya wuce gida wajen iyaye.

Hakkin mallakar hoto
Muhammad Abdu

Haka ma a lokacin da cutar Ebola ta addabi duniya, an bai wa Abdurrazak sunan cutar, dan damben Kudu wanda ya yi fice a wasan.

More News

Gwamnatin Adamawa Ta Ƙara Hutun Ɗaliban Makarantu Saboda Annobar Cutar Ƙyanda

Gwamnatin jihar Adamawa ta tsawaita lokacin komawar É—aliban jihar makarantunsu domin fara  zangon karatu na uku saboda annobar cutar Æ™yanda. A wata sanarwa ranar Litinin,...

Sojan Jamhuriyar Nijar sun kama Gawurtaccen ÆŠan Fashin dajin Najeriya Kachalla Mai Daji

Dakarun sojan Jamhuriyar Nijar sun samu nasara kama gawurtaccen É—an fashin dajin nan mai suna Kachalla Mai Daji a garin Illela dake kan iyakar...

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraÉ—iyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...