Gwamnatin Najeriya Ta Kafa Kwamitin Shirin Dakile Ebola



Gwamnatin Tarayya ta kafa Kwamitin Musamman na Shugaban Kasa domin shirin dakile yaduwar cutar Ebola a Najeriya.

Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Femi Gbajabiamila, ne ya kaddamar da kwamitin ranar Alhamis a Abuja.

Ya ce an dauki matakin ne domin Najeriya ta fara shirye-shiryen kariya tun kafin a samu bullar cutar a kasar, domin kauce wa irin matsalar da aka fuskanta a shekarar 2014.

Gbajabiamila ya bayyana cewa a halin yanzu babu rahoton bullar Ebola a Najeriya, amma gwamnati na son daukar matakan kariya tun da wuri.

Ya kara da cewa an kafa wasu kungiyoyi da za su rika kula da sa ido kan cututtuka, iyakokin kasa da kuma matakan gaggawa.

Haka kuma gwamnatin ta ce an kara tsaurara binciken lafiya a manyan hanyoyin shiga kasar nan, ciki har da filayen jiragen sama da iyakokin kasa.

More from this stream

Recomended