Coronavirus: WHO ta yaba aikin Najeriya | BBC Hausa

Shugaba Muhammadu Buhari

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Shugaban WHO ya ce “Najeriya na yunkuri mai amfanin gaske wurin dakile yaduwar coronavirus

Tedros Adhanom Ghebreyesus, wanda shi ne Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya WHO, ya yaba wa yadda Najeriya ke aikin dakile annobar cutar nimfashi ta coronavirus.

Shugaban ya bayyana haka ne a shafinsa na Twitter biyo bayan rahoton da hukumar kiyaye yaduwar cutuka ta Najeriya ta wallafa irinsa na farko a kasar kan yaduwar kwayar cutar.

“Muna godiya ga hukumar NCDC da gwamnatin Najeriya kan yadda suka zayyana yaduwar cutar COVID19 a kasar,” Tedros Adhanom ya fada.

Ya kara da cewa “wannan shi ne aiki karara na bayar da hadin kai kuma mai amfanin gaske wurin dakile coronavirus daga ci gaba da yaduuwa”.

Najeriya ta tabbatar da rahoton bullar cutar coronavirus ranar 27 ga watan Fabarairun 2020 a asibitin Yaba da ke Legas.

A sanarwar da ya fitar, Ministan Lafiya na Najeriya, Dr Osagie Ehanire, ya ce wani dan kasar Italiya ne da ke aiki a kasar ya shigo da cutar bayan ya dawo Lagos daga birnin Milan.

Hanyoyi 4 na kare kai daga coronavirus

â–  Ku wanke hannayenku da sabulun gargajiya ko sabulun ruwa da ake wanke hannu da shi, wato hand gel, wanda zai iya kashe kwayoyin cuta

â–  Ku rufe hanci da bakinku lokacin da kuke yin atishawa da kyallen fyace majina – sannan ku wanke hannayenku bayan kun yi atishawa domin hana kwayoyin cutar yaduwa.

â–  Ku guji taba idanunku, ko hanci ko bakinku- idan hannunku ya taba wurin da cutar ta shafa, za ta iya yaduwa zuwa sauran sassan jikinku.

â–  Kada ku rika matsawa kusa da mutanen da ke yawan atishawa ko tari da masu fama da zazzabi – za su iya watsa cutar cikin iska ta yadda ku ma za ku iya kamuwa da ita. – akalla ku matsa nesa da su ta yadda tazarar da ke tsakanin ku za ta kai kafa uku.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa É—aya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faÉ—a tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...