Bukatu huɗu cikin shida da ɓangaren Wike su ka gabatarwa da shugabancin jam’iyar PDP

Da alama dai rikicin da jam’iyar PDP take fama da shi na neman zama gobara daga Kogi biyo bayan kin amincewa da bukatun bangaren gwamnan jihar Rivers, Nyesom Wike da shugabannin jam’iyyar su ka yi.

Biyo bayan zaɓen fidda gwani na dan takarar shugaban kasa da kuma zaɓen wanda zai marawa Atiku baya aka fara takun saka tsakanin gwamnan na Rivers da kuma jam’iyar sa ta PDP.

A wata tattaunawa da ya yi da gidan rediyon BBC Hausa sakataren jam’iyar, Umar Tsauri ya ce bukata baza su aiwatu ba.


Sanata Tsauri ya ce akwai buƙatu shida da Nyesom Wike ya gabatar amma ya shaida wa BBC guda huɗu da suka haɗa da:


1-Neman a sauke Iyorchia Ayu daga Shugabancin PDP – “ba za a ce ba zai yiwuwa amma yinsa ba dai-dai bane saboda lokaci”.


2-Atiku ya sa hannu cewa zai yi zangon mulki guda wanda a cewar Sanata Tsauri “babu wanda zai rubuta takarda ya ce zangon mulki daya zai yi.”


3-Buƙatar a janye gwamna Ifeanyi Okowa a matsayin wanda zai marawa Atiku Abubakar a zaɓen shugaban ƙasa na 2023.


4-Sannan neman idan an tashi rabon muƙamai a basu (ɓangaren gwamna Wike) na shugaban ƙasa.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...