Atiku ya ziyarci Hayatudeen a gidansa dake Lagos

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar kuma wanda zai yiwa jam’iyar ADC takara a zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027 ya ziyarci,Muhammad Hayatudeen a gidansa dake Lagos.

Hayatudeen na ɗaya daga cikin waɗanda suka tsaya takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyar ta ADC kafin daga bisani ya janye takararsa dai-dai lokacin da ake tsaka da gudanar da zaɓen fitar da gwani na jam’iyyar.

Da yake bayyana dalilan nasa na janyewa tare da yin watsi da sakamakon zaɓen ya ce an yi aringizon kuri’a tare da saɓa kaidoji yayin gudanar da zaɓen.

Ziyarar da Atiku ya kai masa na zuwa ne biyo bayan makamanciyar ta da ya kai wa tsohon gwamnan jihar Ribas Rotimi Amaechi wanda ya shima ya yi fatali da sakamakon zaɓen.

A cikin wani sako dake ɗauke da hotunan ziyarar da ya wallafa, Atiku ya ce ziyarar ta mayar da hankali ne kan samar da haɗin kai a jami’iyar da kuma tafiya tare da kowa domin karfafa jam’iyyar.

More from this stream

Recomended