Mutane biyu dake takarar shugabancin majalisar wakilai ta tarayya Aliyu Betara da Yusuf Gagdi sun janye takararsu inda suka goyi bayan Tajuddeen Abbas wanda shi ne É—antakar da jam’iyar APC ta tsayar.
Betara da Gagdi sun amince sun janye takarar ta su bayan sun gana da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da mataimakinsa, Kashim Shettima a ranar Lahadi.
A kwanakin baya ne jam’iyar APC ta fitar da sunan Abbas da kuma Benjamin Kalu a matsayin wanda za su jagoranci shugabancin majalisar wakilai ta 10.
Wasu daga cikin Æ´aÆ´an jam’iyar ta APC ciki har da mataimakin shugaban majalisar, Idris Wase sun ki amincewa da zabin na Abbas.
Da yake magana bayan ganawar, Shettima ya yaba musu kan janye war da suka yi inda ya ce shugaban ƙasar ya ji dadin matuka da janyewar ta su.