Biyu Daga Cikin Masu Takarar Shugabancin Majalisar Wakilai Sun Janyewa Tajuddeen Abbas

Mutane biyu dake takarar shugabancin majalisar wakilai ta tarayya Aliyu Betara da Yusuf Gagdi sun janye takararsu inda suka goyi bayan Tajuddeen Abbas wanda shi ne É—antakar da jam’iyar APC ta tsayar.

Betara da Gagdi sun amince sun janye takarar ta su bayan sun gana da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da mataimakinsa, Kashim Shettima a ranar Lahadi.

A kwanakin baya ne jam’iyar APC ta fitar da sunan Abbas da kuma Benjamin Kalu a matsayin wanda za su jagoranci shugabancin majalisar wakilai ta 10.

Wasu daga cikin Æ´aÆ´an jam’iyar ta APC ciki har da mataimakin shugaban majalisar, Idris Wase sun ki amincewa da zabin na Abbas.

Da yake magana bayan ganawar, Shettima ya yaba musu kan janye war da suka yi inda ya ce shugaban ƙasar ya ji dadin matuka da janyewar ta su.

More News

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...

Manyan dillalan mai za su fitar da litar man fetur miliyan 300 a wannan makon

Ƙungiyar MEMAN ta manyan dillalan man fetur da dangoginsa ta ce mambobinta sun fara lodin mai har lita miliyan 300 a cikin makon nan...

Kotu ta É—aure mutumin sa ya yi sama-da-faÉ—i da kuÉ—in marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...