Bayan kammala sanya farar Tuta mai ɗauke da rubutun ‘Muhammadurrasulullah’ a taron saka Tuta da aka yi a jiya Laraba 30/10/2019 daidai da 1l3l1441, a Husainiyyatul Mahadi (atf) Sakkwato, Tutar wacce take alamta kamawar watan da aka haifi Annabin Rahama SAW ‘Rabi’ul Awwal’.
Wakilin ‘yan Shi’a almajiran Zakzaky Malam Sidi Munir Sakkwato ya gabatar da taƙaitaccen jawabi dangane da maƙasudin taron, ya kuma taya murnar zagayowar wannan wata mai albarka na Rabi’u awwal ga ɗaukacin jama’a maharta taron, a lokaci ɗaya kuma ya taya jaje kasantuwar a irin wannan ranar ce ta 1 ga watan Rabi’ul awwal aka yi karon batta tsakanin rundunar Sojan Najeriya da ‘yan Shi’a a Zariya a lokacin bukin sanya Tuta.
Malamin ya cigaba da bayani dangane da karamomi da mu’ujizoji na fiyayyen halitta Annabi Muhammad. Haka Kuma ya yi magana dangane da halin da Zakzaky da Zeenatu suke ciki tun bayan dawowa daga kasar Indiya.
A karshe Malam Munir ya ƙarƙare da kira tare da ƙarfafa ‘yan Shi’a dangane da fita neman ‘yancin Jagoran su Zakzaky musamman a Abuja, sannan ya yi kira ga ‘yan Shi’an akan su cigaba da dukkanin shirye-shiryen da suka kamata don halartar Muzaharar Maulidin bana a Abuja kamar yadda aka saba yi a Zariya a lokacin da Zakzaky yake waje, “lalle babu wani sassauci tsakaninmu da gwamnati matsawar zasu cigaba da riƙe jagoran mu musamman a wannan hali da yanayi da suke ciki na rashin lafiya shi da mai ɗakinsa”.