Atiku, Tinubu da Osinbajo sun hadu a wurin daurin aure a Abuja – AREWA News

Daurin auren, Isma’il Ribadu ranar Asabar a birnin tarayya Abuja , ya hada manyan yan siyasa da dama da suka fito daga jam’iyun APC da PDP.

Isma’ila ɗa ne ga Mallam Nuhu Ribadu tsohon shugaban hukumar EFCC na farko kuma tsohon dan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar ACN a zaben 2011.

Daga cikin manyan bakin da suka halarci daurin auren sun hada da mataimakin shugaban kasa, Yemi Osinbajo, tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da kuma Bola Ahmad Tinubu jagoran jam’iyar APC na kasa.

Shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Mallam Abba kyari, gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari, ministan sadarwa, Dakta Isa Ali Ibrahim Pantami da kuma tsofaffin gwamnonin Sokoto da Ogun, Aliyu Wamakko da Ibikunle Amosun suma sun halarci taron.

An daura auren ne a masallacin Annur dake birnin tarayya,Abuja.

Ga wasu daga cikin hotunan taron daurin auren:

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...