APC Ta Ɗage Zaɓen Fidda Gwani A Bauchi Da Kwara



Jam’iyyar APC ta sanar da ɗage zaɓen fidda gwani na gwamna a jihohin Bauchi da Kwara zuwa ranar Juma’a, 22 ga watan Mayu, 2026.

Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da kwamitin gudanarwa na ƙasa na jam’iyyar ya fitar ranar Alhamis.

Jam’iyyar ta kuma tsawaita zaɓen fidda gwani na kujerun majalisar dokokin jihar Zamfara na mazaɓun Maradun ta ɗaya da Maradun ta biyu zuwa ranar Lahadi, 24 ga watan Mayu.

APC ta ce an amince da sauyin jadawalin ne bayan tattaunawa da masu ruwa da tsaki domin tabbatar da gudanar da zaɓe cikin gaskiya, lumana da tsari.

Jam’iyyar ta bayyana cewa sauyin ya shafi zaɓen gwamna a Bauchi da Kwara da kuma kujerun majalisar dokokin jihar Zamfara kawai.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]