An shiga zaman zullumi bayan da aka zargi jami’an hukumar tsaro NSCDC wato Civil Defence da harbe wata mata a filin sallar Idi dake Gusau a jihar Zamfara.
Jami’an na Civil Defence sun buÉ—e wuta ne lokacin da suka biyo wasu É“ata gari a wajen sallar Idin inda harsashi ya yi kuskuren samun matar.
Daga bisani wasu matasa da suka fusata sun Æ™ona wata mota Æ™irar Hilux ta da jami’an tsaron suka zo da ita tare da jikkata wasu daga ciki.
Mai magana da yawun rundunar Æ´an sandan jihar Zamfara, Yazid Abubakar ya ce jami’an suna tsare da jami’an NSCDC guda biyu a hannunsu inda ya Æ™ara da cewa ana cigaba da bincike kan lamarin.