An tsaurara matakan tsaro a kotun da ake shari’ar zaben shugaban ƙasa

Jami’an tsaro dauke da makamai sun killace tituna zuwa kotun shari’ar zaben shugaban kasa a ranar Laraba da ke Abuja.

An gindaya shingayen binciken ababen hawa guda uku tsakanin hedkwatar ma’aikatar kudi da kofar kotun.

Ana sa ran kotun za ta yanke hukunci kan koke-koken zaben da ke kalubalantar zaben shugaba Bola Tinubu da ‘yan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Peoples Democratic Party, Atiku Abubakar, da kuma Peter Obi na jam’iyyar Labour Party suka yi.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]