Gwamnatin rikon-kwarya ta Sudan ta kafa dokar-ta-baci a yankin gabashin kasar, bayan wani rikicin kabilanci ya yi sanadiyyar mutuwar mutane akalla 16.
Haka kuma gwamnatin ta wucin-gadi ta kori gwamnan jihar Red Sea, tare da babban jami’in tsaro na yankin.
Ba a dai san ainahin abin da ya haddasa rikicin ba, zuwa yanzu.
Wata sanarwa ta gwamnati ta ce a karon farko a irin wannan rikici, an yi amafani da bundugogi, abin da ke nuna alamun sanya hannun wasu na ciki da wajen kasar domin rura wutar rikicin.
A ‘yan kwanakin nan ne dai Sudan din ta fito daga rikici na wata da watanni,
inda aka yi yarjejeniyar kafa gwamnatin riko ta raba iko tsakanin farar-hula da soji, bayan kawar da gwamnatin dadadden shugaban kasar Omar al-Bashir.
Daga cikin muhimman ayyukan da ya fara sabon Firaministan kasar ya ce ya fara tattaunawa da Asusun Lamuni na Duniya IMF, da Bankin Duniya a wani yunkuri na sake fasali ga dimbin bashin da ake bin Sudan din.
A yayin wata hira da kamfanin dillacin labarai na Reuters Abdallah Hamdok ya ce Sudan tana kuma neman tallafin dala biliyan 8 daga kasashen duniya nan da shekara biyu, da kuma wani tallafin gaggawa a yanzu domin karfafar darajar kudin kasar.
Tashin farashin mai da na abinci ne dai suka haifar da zanga-zanga a watan Disamba, abin da ya yi sanadin hanbarar da Shugaba Omar Albashir, wanda yanzu yake fuskantar shari’a a kasar.