An kashe makiyaya biyu a jihar Plateau

Makiyaya biyu mace da namiji aka bada rahoton an kashe su a wajejen garin Tahore dake ka karamar hukumar Bokkos ta jihar Plateau.

Wasu makiyaya dake yankin sun ce an kashe makiyayan ne a wani kwanton bauna da aka yi musu aka harbe su lokacin da suke kan hanyarsu ta dawowa daga kasuwar Maikatako akan baburdinsu.

Shugaban kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) na jihar, Ibrahim Yusuf Babayo wanda ya tabbatarwa da yan jaridu faruwar lamarin a Jos ya ce lamarin ya faru ne da maraice.

Shugaban na MACBAN  ya bayyana sunayen Umar Saidu da Rashida Yakubu a matsayin wadanda aka kashe.

Da yake allawadai da kisan ya yi kira ga jami’an tsaro da su gaggauta daukan matakai  domin kaucewa hare-hare na ramuwar gayya a yankin na Bokkos.

Babayo ya yi kira ga Fulani makiyaya da kada su dauki doka a hannunsu.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan YaÆ™i Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin Æ™wazon jagorancinsa wajen yaÆ™i da ta’addanci da magance matsalar tsaro a Æ™asar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiÆ™a da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]