Rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen jihar Taraba, NPF, ta tabbatar da kashe wasu ‘yan bindiga biyu a Jalingo, babban birnin jihar.
‘Yan ta’addar, wadanda rundunar ta ce adadinsu ya kai 40, an ce sun kai hare-hare ne a wani dakin ajiyar kaya mallakar wani mai suna Jugulde da sanyin safiyar Asabar.
Baya ga ma’ajiyar kayayyaki, an kuma tabbatar da cewa ‘yan bindigar sun kai hari kan shaguna da ofisoshi da dama.
Daga cikin shaguna da ofisoshin da aka lura an kai musu hari sun hada da ofishin gidan rediyon Rock FM, wanda ke kan titin Mallam Joda a cikin babban birnin Jalingo.