An halaka mutane 6 a wani faɗa tsakanin ƴanbindiga da ƴanbanga

Mutane 6 ne suka rasa rayukansu a wata arangama da aka yi tsakanin ‘yan bindiga da ’yan banga da aka fi sani da ‘Yan Sakai a karamar hukumar Gada a jihar Sakkwato.

‘Yan bangar, a cewar wata majiya a yankin da ta nemi a sakaya sunanta saboda yadda lamarin ya kasance, an ce sun dauki fansa ne kan kisan da wasu ‘yan bindiga suka yi wa shugabansu, Alhaji Dahiru.

Shaidun gani-da-ido sun ce rikicin ya fara ne a lokacin da wani jagoran ‘yan banga kauyen Gidan Hashimu ya yi wani yunkuri na kama wasu barayin shanu.

Rahotanni sun ce ‘yan bindigar da ake zargin, a daidai lokacin da rikicin ya yi kamari, sun harbe shugaban ‘yan bangan har lahira, lamarin da ya janyo ramuwar gayya daga ‘yan banga.

Daya daga cikin shaidun gani da ido ya ce kafin isowar tawagar jami’an tsaron kasuwar, sama da mutum shida ne suka mutu.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani ɓangare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...