Wasu fusatattun matasa da ke Kofar Kabuga da ke a Jihar Kano sun ƙone wani a-daidaita-sahun da ake zargin cewa an yi amfani da shi wajen ƙwacen waya.
Rahotannin da muka samu sun nuna cewa waɗanda suke cikin a-daidaita-sahun sun samu sun tsere.
Wannan lamari dai ya faru ne a daren jiya Asabar.
Matsalar ƙwacen waya da kashe mutane dai ya yi ƙamari a Arewacin Najeriya musamman Kano, inda kusan kullum sai an samu rahotannin aikata wannan mummunan aiki.