
Rotimi Amaechi dake neman jam’iyar ADC ta tsayar da shi takarar shugaban ƙasa a zaben shekarar 2027 ya yi watsi da sakamakon zaɓen fitar da gwani da a jam’iyyar ta gudanar.
A ranar Litinin jam’iyar ADC ta gudanar da zaɓen yar tinke domin fitar da wanda zai yiwa jam’iyyar takarar shugaban ƙasa a zaben da aka gudanar da shi a faɗin Najeriya.
Yan takara uku ne suka shiga zaben da su ka haɗa da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, tsohon gwamnan jihar Ribas Rotimi Amaechi da kuma Muhammad Hayatu Deen.
A wata sanarwa da ya fitar ranar Talata Amaechi ya yi zargin tafka magudi a zaɓen da kuma hana wasu mutane damar kaɗa kuri’a a yayin zaɓen inda ya ƙara da cewa sakamakon da ake fitarwa ƙirƙirar sa aka yi.
Ya kara da cewa ba zai karbi sakamakon da ya saɓa da irin halaye da dabi’u da jam’iyar ADC ta ci alwashin dabbaƙawa.
Ya ce babu ta yadda za ayi ya karɓi sakamakon zaɓen da aka hana kaso 80 na ƴan jam’iyyar damar shiga su zaɓi wanda su ke so.

