Abu biyar da ba ku sani ba game da ƙasurgumin ɗan fashin Zamfara Bello Turji

Asalin hoton, Daily Trust

Bayanan hoto,
“Mahaifiyar Kacalla Turji mai suna ‘Yar Kagara ta guje shi har ma ba ta so a ambaci sunansa.”

Sunan Bello Turji ya karaɗe wasu sassa na Najeriya musamman a arewa maso yamma sakamakon masarautar fashi da makami da ya kafa a dazukan jihohin Zamfara da Sokoto.

Garuruwa da dama da suka haɗa da Isa na Sokoto da kuma yankunan Ƙaramar Hukumar Shinkafi na Zamfara na daga cikin yankunan da Turji ya mayar kamar masarautarsa, inda yake sace mutane don karɓar kuɗin fansa da kuma kashe ko barin waɗanda ya ga dama.

Kazalika, basaraken ɗan fashin da mayaƙansa kan karɓi harajin amfanin gona daga mazauna yankunan, wasu lokutan kuma sukan ƙona gonakin idan mutanen suka yi gardama.

Sai dai rahotanni sun nuna cewa ƙasurgumin ɗan fashin na neman yin sulhu da gwamnati har ma ya sako mutum fiye da 50 da ya yi garkuwa da su a watannin baya. Kodayake ‘yan sanda sun ce mutum 97 ne kuma su suka ceto su.

Wane ne Bello Turji? Su wane ne abokan aikinsa? BBC Hausa ta tattauna da Dr. Murtala Ahmad Rufai, malami a Sashen Tarihi na Jami’ar Usmanu Danfodiyo Sokoto, wanda ya yi bincike kan ayyukan ‘yan fashi kuma marubucin littafin ‘I am a Bandit’.

An haifi Muhammadu Bello wanda aka fi sani da Kacalla Turji a yankin Ƙaramar Hukumar Shinkafi da ke cikin Jihar Zamfara a yanzu.

Sai dai yankin na Shinkafi da kuma garuruwan Isa da Sabon Birni na Jihar Sokoto ƙasa guda ce a shekarun baya, abin da ke nufin babu tabbas kan takamaimiyar jihar da aka haife shi.

“A Shinkafi ya taso kuma a nan ne mahaifnsa ke zuwa da shi cin kasuwar dabbobi da sauransu kamar kowane Bafulatani,” in ji Dr. Murtala.

Binciken da masanin ya yi ya nuna cewa shekarun Turji sun kama daga 27 zuwa 35.

“Shi ma mahaifinsa Usman wanda aka fi sani da Mani na Marake ɗan asalin yankin ne, mai arzikin dabbobi, kuma mutum ne bawan Allah da ke da tarihi na zaman lafiya tsakanin manoma da makiyaya.”

Mahaifyarsa kuma, an fi saninta da ‘yar Kagara – ta yankin Shinkafi – wadda ke da alaƙa da babban yaron Turji mai suna Danbokolo.

Uwa da uba da ‘yan uwan Turji sun guje shi

Bayanai sun nuna cewa baki ɗayan ‘yan uwan Turji ba sa hulɗa da shi sakamakon sana’arsa ta fashi da makami.

Hakan ta sa mahaifinsa Mani na Marake ya yi hijira zuwa garin Kura na Jihar Kano, daga baya ya koma Jigawa, kamar yadda Murtala ya tabbatar.

A watan Yulin 2021 an samu rahotanni cewa ‘yan bindigar da ke biyayya ga Turji sun fantsama garuruwan yankin Shinkafi tare da sace mutane da yawa a matsayin martanin kama mahaifin nasa da aka yi.

“Ya yi iya bakin ƙoƙarinsa (mahaifin Turji) don ya hana shi amma ya ƙi ji, saboda haka ya tashi daga Zamfara ya koma Kano.

“Ita kuma ‘Yar Kagara (mahaifiyar Turji) ba ma ta son a ambaci sunansa. Kuma mutanen da ke wurin sun shaide ta da cewa lamarin ya fi ƙarfinta da kuma mahaifinsa.

“Yan uwansa na kusa da na nesa ba su da alaƙa da shi, ba sa karɓar duk wani abu da ya fito daga hannunsa na kuɗi ko kyauta saboda ba wanda ya yarda da abin da yake yi – idan ka cire Ɗanbakolo.”

Turji ya yi karatun Islamiyya

“Tabbas Bello Turji ya yi karatun Islmaiyya kuma yana da ilimi gargwado, amma ba ilimi mai zurfi ba kamar yadda mutane ke tunani,” a cewar malamin jami’ar.

Haka nan jagoran ‘yan fashin ya yi karatun boko, inda bayanai suka nuna cewa ya kammala firamare.

Yaran Turji ba talakawa ba ne,akwai ‘ya’yan manya

Manyan yaran da Turji ke jagoranta matasa ne masu shekaru irin nasa, waɗanda daga cikinsu akwai ‘ya’yan sarakuna da hakimai a yankin.

Dr. Murtala ya lissafa wasu daga cikinsu waɗanda mafi yawansu abokansa ne da suka taso tare.

  • Kacalla Ɓingyal – mutumin Kagara
  • Ɓaleri – mutumin Sakai
  • Alhaji Auta
  • Bello Kagara
  • Yalo Ɗanbokolo – ɗan uwan Turji na jini kuma babban yaronsa
  • Malam Ila Manawa
  • Yalo Emiya
  • Abdullahi – mutumin Kagara
  • Umaru Nagona – mutumin Kagara

“Misali, akwai Ila Manawa wanda mahaifinsa mai garin Manawa ne, yana cikin manyan yaran Turji.

“Duk waɗannan yaran ba talakawa ba ne, suna da hali da duk abin da kake tunani – dukiya a wajensu ita ce shanu.

“Kuma dukkansu suna ɗauke da makamai a yanzu.”

Bai daɗe da zama ɗan fashi ba

Dr. Murtala ya ce Bello Turji bai daɗe da fara satar shanu da kuma kashe-kashen mutane ba.

“Ko a lokacin da wannan rikici ya fara a Zamfara lokacin su Tsoho, wanda aka fi sani da Buharin Daji, Turji na ƙarami kuma bai shiga wannan aƙidar ba. Daga baya ya shige ta,” a cewarsa.

“Gabagaɗi ya shiga harkokin, duk waɗanda ke yankin za su faɗa muku cewa lokacin da ake yi (a wancan lokacin) kasuwa yake zuwa.”

[ad_2]

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...