

Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON) ta sanar da cewa ƙasar Saudiyya ta ƙi amincewa da buƙatar Najeriya na ƙarin kujerun Hajj a shekarar 2027, inda ta bar adadin da aka ware wa ƙasar ba tare da canji ba duk da ƙaruwa da aka samu ta buƙatar masu niyyar yin aikin Hajji daga sassa daban-daban na ƙasarnan.
Hukumar ta bayyana cewa ta yi mu’amala da Ma’aikatar Hajji da Umrah ta Saudiyya a hukumance, tana neman ƙarin kujeru domin sauƙaƙa wa yawan Musulmin Najeriya da ke son yin wannan tafiya mai tsarki, da kuma amsa roƙon hukumar jin daɗin alhazai ta jihohi da ke neman ƙarin kujeru.
Sai dai hukumomin Saudiyya sun bayyana cewa ba za su iya bayar da ƙarin kujeru ba saboda matsalolin girman wuraren ibadan da kuma manufar ƙasar na bin ƙa’ida wajen raba kujeru ga kowace ƙasa bisa tsarin da ake aiki da shi yanzu.
Saboda haka, adadin da aka ware wa Najeriya a aikin Hajjin 2027 ya tsaya ne a kujeru 35,000 ga alhazai na gwamnati da kuma kujeru 15,000 na kamfanoni shirya tafiye-tafiye da aka yi wa lasisi, wanda hakan ya kai jimillar kujeru 50,000.
Shugaba kuma babban darakta na NAHCON, Ambasada Ismail Abba Yusuf, ya ce hukumar ta fahimci takaicin da wannan hukunci zai iya haifar wa masu niyyar yin Hajji da hukumomin alhazai na jihohi da suka yi fatan samun ƙarin kujeru.
Ya bayyana cewa Hukumar ta yi amfani da dukkan hanyoyin diflomasiyya da na aiki wajen neman ƙarin kujeru, amma tana girmama hukuncin ƙarshe na hukumomin Saudiyya.
“Mun fahimci ƙaunar da zukatan yawancin Musulmin Najeriya suke da shi na yin Hajji da kuma tsammanin jihohi da masu ruwa da tsaki da ke neman ƙarin kujeru. Duk da ƙoƙarin da aka yi don samun ƙarin kujeru, hukumomin Saudiyya sun bayyana matsayinsu na ƙarshe bisa ga gaskiyar aiki da iyakokin ƙarfin wuraren ibada,” in ji Ambasada Yusuf.
Shugaban NAHCON ya yi kira ga hukumomin jin daɗin alhazai na jihohi, hukumomi da masu gudanar da kamfanonin tafiye-tafiye a lasisi su yi amfani da kujerun da aka ware musu cikin adalci da gaskiya tare da bin ƙa’idojin da hukumar ta gindaya da kuma tsarin Nusuk na Saudiyya.