
Aƙalla mutum 60 sun rasu bayan da wata mahakar zinare ta rufta a jihar West Kordofan da ke Sudan.
Wani mutum da ya tsira daga lamarin ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labaran Faransa (AFP) cewa wasu mutane da dama sun ɓace bayan ruftawar mahakar, yayin da har yanzu ba a tabbatar da ko sun makale a ƙarƙashin baraguzan ginin ba.
Masu aikin ceto na ci gaba da ƙoƙarin gano gawarwaki da kuma ceton mutanen da ake kyautata zaton suna raye a cikin mahakar Al Zaara, da ke kusa da birnin El Nahud.
Ruftawar mahakar ma’adanai na yawan faruwa a Sudan, musamman a wuraren da ake gudanar da aikin hakar ma’adanai ba tare da cikakken tsaro ba.