Dakarun Najeriya Sun Kuɓutar Da Mutane 31 Daga Hannun ’Yan Bindiga A Katsina Da Kebbi

Muhammadu SabiuHausa22 minutes ago



Dakarun Rundunar Fansan Yamma da ke gudanar da ayyukan tsaro a yankin Arewa maso Yammacin Najeriya sun ce sun kuɓutar da mutane 31 da ’yan bindiga suka yi garkuwa da su a jihohin Katsina da Kebbi.

Rundunar ta kuma ce dakarunta sun kama wasu mutane biyu da ake zargi ’yan ta’adda ne, tare da ƙwato alburusai, wasu kayan aikin kai hari, babur da kayan sarki.

A wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na rundunar, Laftanar Kanar Aliyu Ɗanja, ya fitar, ya ce dakarun haɗin gwiwar sun gudanar da ayyukan tsaro a jihohin biyu a ranakun Litinin da Talata.

A Katsina, dakarun sun kuɓutar da mutane 10, da suka haɗa da maza uku da mata bakwai, bayan samun kiran neman agaji kan sace su a ƙauyukan Unguwar Daudu da Unguwar Ci-ɓauna da ke ƙaramar hukumar Funtuwa.

A jihar Kebbi kuwa, rundunar ta ce bayan samun sahihan bayanan sirri, dakarunta sun kai samame a ƙauyukan Fafala da Dadikwa da ke ƙaramar hukumar Kangiwa.

Rundunar ta ce musayar wuta tsakanin dakarunta da ’yan ta’addan ta tilasta wa ƴan bindigar tserewa, lamarin da ya ba dakarun damar kuɓutar da wasu mutane 21.

Haka kuma, dakarun sun kama wasu mutane biyu da ake zargi da ta’addanci a yankin Ƴantumaki na ƙaramar hukumar Ɗan Musa a Katsina. A cewar rundunar, binciken farko ya nuna cewa waɗanda ake zargin suna da alaƙa da wani ɗan ta’adda mai suna Mannori.

Sai dai yayin da rundunar ke bayyana nasarorin, wasu masana harkokin tsaro na ganin akwai buƙatar dakarun Najeriya su ƙara matsa lamba kan masu aikata laifuka tare da kai ayyukan sintiri da farmaki cikin dazuzzukan da ake zargin ’yan bindiga na fakewa, domin dakile ayyukansu.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...