Wani Mutumi Ya Bayyana Yadda Ya Gano Ana Zargin Matarsa Da Cin Zarafin ‘Yarsu

Muhammadu SabiuHausa15 minutes ago



Mijin wata mata mai shekaru 36, Anulika Onyeanyusi, wadda ‘Yan Sandan Jihar Anambra suka kama bisa zargin cin zarafin ‘yarta karamar yarinya, ya bayyana yadda ya gano lamarin.

Ikechukwu Onyeanyusi ya ce wani abokinsa ne ya sanar da shi abin da ake zargin matarsa ta aikata, bayan ya nuna masa wani bidiyo da ake zargin yana nuna matar tana amfani da abin wasan jima’i wajen cin zarafin ‘yarsu.

Ya ce yana dawowa daga wajen sana’arsa ne da yammacin ranar Alhamis lokacin da abokin nasa ya kira shi tare da nuna masa bidiyon.

A cikin wani bidiyo da Ma’aikatar Harkokin Mata da Jin Dadin Al’umma ta Jihar Anambra ta wallafa a shafinta na Facebook ranar Asabar, Onyeanyusi ya ce bai taba ganin bidiyon a kafafen sada zumunta ba kafin abokinsa ya nuna masa.

Onyeanyusi ya ce daga baya ya tambayi matarsa game da bidiyon, amma ta musanta cewa abin da ke cikinsa gaskiya ne, tana mai cewa an kirkire shi ne ta amfani da fasahar AI.

Ya ce ya tambaye ta yadda za ta musanta abin da ya gani da idonsa, amma ta ci gaba da cewa bidiyon ba na gaskiya ba ne.

Ya kara da cewa ya koma wajen abokinsa domin ya sanar da shi bayanin da matarsa ta yi, tare da tambayar ko da gaske zai yiwu a kirkiri irin wannan bidiyo ta hanyar AI.

A cewarsa, jim kadan bayan haka ‘yan sanda suka isa gidansa domin bincike, kafin daga bisani su kama matarsa.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...