

Gwamnan Borno, Babagana Zulum, ya ce sama da makarantu 5,000 ne aka lalata sakamakon ta’addanci a jihar.
Zulum ya bayyana haka ne a ranar Lahadi yayin bikin kaddamar da wasu ayyuka a Maiduguri, babban birnin jihar,ya bayyana cewa kimanin yara miliyan 2.2 ne ba sa zuwa makaranta a jihar.
“Ina so in bayyana cewa ta’addanci ya lalata sama da makarantu 5,000, kuma a lokacin da matsalar ta kai kololinta, yara miliyan 2.2 ba sa zuwa makaranta, inda ƙasa da yara 500,000 ne kawai ke yin rajista,” in ji shi.
“Malamai da dama da shugabannin makarantu sun rasa rayukansu a yayin gudanar da aikinsu.”
Ya ce yau an kaddamar da muhimman ayyuka guda hudu: Larawaram Community Senior Secondary School; Shehu Sanda Kyarimi I Primary and Junior Secondary School; gadar post office mai tsawon 9-span; da kuma titin kilomita 2.5 tare da magudanan ruwa na kilomita 5 daga Budum Tandari Junction zuwa Kasuwan Shanu.
Zulum ya ce sake gina makarantu ba wai kawai gina gine-gine ba ne, face “komawa ga samar da damar ilimi, dawo da kwarin gwiwa a cikin al’umma, da kuma ba wa yara damar samun kyakkyawar makoma.”
Ya bayyana cewa tsakanin shekarun kasafin kuɗi na 2025 da 2026, gwamnatin ta zuba biliyoyin kuɗi a fannin ilimi da suka kai naira biliyan 46.9.
A cewarsa, wannan kaddamarwa na cikin manyan jarin da aka yi, tare da ayyuka 136 da aka kammala kuma ake jiran a ƙaddamar da su.
Gwamnan ya ce gwamnati ta ci gaba da faɗaɗa da inganta gine-ginen makarantu a matakin firamare.
Adadin ajujuwan da ake iya amfani da su ya karu zuwa 5,792, yayin da wuraren tsafta da ruwa (WASH) suka karu zuwa 4,563. A matakin sakandare, adadin makarantu masu aiki ya karu daga 34 a cikin ƙananan hukumomi 8 a shekarar 2019 zuwa 129 a cikin ƙananan hukumomi 25 a 2026.
Rajistar ɗalibai ta karu daga 766,551 a 2019 zuwa 1,801,295 a 2026, wanda ke nuna ƙarin ɗalibai sama da miliyan ɗaya cikin shekaru bakwai.
Zulum ya ce wannan ci gaban ya nuna faɗaɗa damar ilimi, ƙara kwarin gwiwar jama’a, da kuma ci gaba da zuba jari a fannin ilimi.