

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya isa ƙasar Faransa domin ci gaba da hutunsa na shekara wanda zai ɗauki makonni uku, bayan ya fara hutun a birnin Landan, Birtaniya.
Emmanuel Ayodele Oke, jakadan Najeriya a ƙasar Faransa ne ya tarbi Tinubu bayan saukarsa a birnin Paris.
Shugaban ya fara hutun ne a ranar 30 ga watan Agusta, kuma ana sa ran zai dawo Najeriya bayan kammala hutun.
Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya bayyana cewa hutun zai kasance “hutu mai haɗe da aiki” inda zai ɗauki lokaci yana yinsa a Turai.
“Matakin farko zai kasance Landan, Birtaniya,” in ji Onanuga lokacin da yake sanar da tafiyar shugaban daga Abuja.
Onanuga ya kuma ce ana sa ran Tinubu zai dawo gida bayan hutun domin shiga shirye-shiryen zaben shekarar 2027.
Hutun shugaban na shekarar 2026 na zuwa ne biyo bayan kammala hutun mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, wanda ya ɗauki makonni biyu.
Stanley Nkwocha, mai taimaka wa mataimakin shugaban ƙasa kan harkokin yada labarai, ya bayyana hutun Shettima a matsayin na farko tun bayan hawansa mulki.
Shettima ya dawo Najeriya a ranar 18 ga watan Agusta, kwana biyu kafin lokacin da aka tsara.
Tinubu ya kuma yi hutu na kwanaki goma a watan Satumba 2025, inda ya ziyarci Birtaniya da Faransa.