
Ministan Tsaro, Christopher Musa, ya bayyana goyon bayansa ga sake zaɓen Shugaba Bola Tinubu da Gwamnan Kaduna, Uba Sani, a zaɓen 2027.
Musa ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin wata ganawa da masu gudanar da harkokin yaɗa manufofin siyasa na GCG Musawah 4 PBAT 2027 a Kaduna.
Taron ya samu halartar masu shirya yaɗa manufofin siyasa daga ƙananan hukumomi 23 na jihar Kaduna, tare da wakilan ƙungiyoyin masu ruwa da tsaki sama da 300.
Ministan ya buƙaci mambobin ƙungiyar da su ci gaba da jajircewa wajen yaɗa manufar sake zaɓen Tinubu da Uba Sani, tare da yin aiki wajen gina Najeriya mai ƙarfi da wadata.
Ya kuma yi kira ga ‘yan Najeriya da su ƙarfafa haɗin kan ƙasa, zaman lafiya da juriya tsakanin mabiya addinai, yana mai cewa ƙwarewarsa ta rayuwa a Sokoto ta koya masa muhimmancin zaman tare.
Musa ya ce Najeriya na da dimbin albarkatun mutane da na ƙasa da za su iya kawo sauyi idan ‘yan ƙasar suka haɗa kai wajen gina ƙasa.